Skip to main content

Zakzaky Ya So Ya Kunyata Nigeria Da Indiya A idon Duniya


Gwamnatin Najeriya ta ce wasu dabi'u da shugaban kungiyar harka Isalamiyya na Najeriya ya nuna a kasar Indiya da ka iya kunyata gwamnatocin Najeriya da India na daga cikin dalilan da suka sanya aka mayar da shi gida.
A ranar Juma'a 16 ga watan Agusta ne dai Sheikh Ibrahim El-Zakzaky ya isa Najeriya bayan yunkurin kula da lafiyarsa da mai dakinsa Zeenat ya ci tura a kasar Indiya.
Malamin dai a cikin wani sako da ya fitar ta faifan bidiyo gabanin komawarsa Najeriya, ya ce yana ganin ba zai samu kulawar da ta dace ba, kasancewar ba a bar shi ya gana da likitocin da suka cancanta ba.
Sannan gabanin hakan ya yi zargin cewa an tsananta tsaro a asibitin da yake zaune, inda ya ce akwai matukar takura ga rayuwarsa.
Me zai faru da Zakzaky bayan da ya koma Najeriya?
Ibrahim Zakzaky ya so bijirewa a Indiya - Gwamnatin Najeriya
Me ya sa 'yan Indiya ke 'maraba' da Zakzaky?
Sai dai bayan komawar malamin Najeriya, kamfanin dillancin labaru na Najeriya ya ruwaito cewa babbar sakatariyar ma'aikatar yada labarun kasar, Mrs. Grace Gekpe ta ce halayyar da Sheikh Zakzaky ya nuna a kasar ta India ne ta sanya dole a mayar da shi gida.
A cewar wata sanarwar da ta fitar "A wani yunkuri na wancakali da ka'idoji na kasa da kasa, jagoran na IMN ya fara tuntubar wasu lauyoyi a Indiya da nufin neman mafaka a kasar".
"Ya kuma tuntubi wasu kungiyoyi masu zaman kansu kamar hukumar kare hakkin dan'adam ta muslunci, da wasu kungiyoyi masu alaka da akidar Shi'a domin ganin ya samu nasarar neman mafakar.
Sanarwar ta yi bayanin cewa inda Sheikh Ibrahim Zakzaky ya samu nasarar samun umurnin kotu a kasar Indiya na neman mafaka, to da hakan ya saba wa ka'idojin da kotu ta gindaya a Najeriya game da shari'ar da ake masa.
Bugu da kari sanarwar ta zargi matar Sheikh Zakzaky, Zeenat, da laifin kokarin haifar da rashin jituwa tsakanin jami'an tsaron Najeriya da na Indiya,  a lokacin da ta zargi jami'an tsaron Najeriya da laifin kisan 'yayanta.
Ita dai gwamnatin Najeriya ta yi kokarin bin umurnin wata babbar kotu ne ta jihar Kaduna, wadda ta amince wa Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da matarsa Zeenat su tafi kasar Indiya domin neman lafiya.
Malamin yana fama ne da rashin lafiya tun bayan kama shi da aka yi da mata

Comments

Popular posts from this blog

Amfanin Ganyen Magarya A Jikin Dan’adam

Itaciyar ganyen magarya ana kiranta da Assidir a Larabce. Itaciya ce mai albarka da kuma dimbin tarihi.  Ya kasance ana amfani da ita tun kamin zuwan addinin Musulunci a duniya, bayan zuwan musulunci a duniya sai malamai da wasu magabata masana ilmin tsirran itatuwa suka bada fatawar amfaninta da irin cututtukan da take magani. Daga bisani suma masana kimiya ba a bar su a bayaba dan sun kaddamar da irin nasu bincike a kan alfanon ganye da kuma diyan magarya. Binciken ya baiwa masana ilimin harhada magani na yankunan turai da wasu yankunan kasahen duniya na Larabawa da India dama nan Afrika wata muhimmiyar damar saka bishiyar magarya a jerin bishiyoyin da ke da karfi da saurin warkar da wasu cututtukka. Ga kadan daga cikinsu:========= -Ciwon daji: A dafa garin magarya a misalin kofi daya karami sai a tarfa zuma mai kyau cokali biyu sai a sha da safe bayan an ci abinci. Amma a sanda ake shan magani irin wannan akwai bukatar a kauce wa shan wasu rukunnan magunnan bature. -Miki ko kura...

YADDA AKE SADUWA DA AMARYA A RANAR FARKO!

Babban abinda yake sa Mata jin tsoron jama’i shine ta yadda ake fara saduwa dasu a lokacin da suka yi auren farko wato lokacin da aka aurar da yarinya tana budurwa. Abinda ya kamata mu sani anan shine lokacin da ango zai kawar da budurcin amaryar sa yakamata ya bita a hankali domin kada ya manta ita amaryar​ batasan yadda akeyin Jima’i ba. ,             YANDDA ANGO YAKAMATA YAYI YAYIN SADUWAR FARKO , An fi son miji yaje ma matarsa da hira kuma kada yayi gaggawar nuna mata cewar yin jimai ya kawo shi kusa da ita, ldan yana cikin hira da ita sai ya kwantar da kansa akan kafafuwanta kuma yaci gaba da hirar sa. , In an dan dauki lokaci ana hira sai ya dauki daya daga cikin hannayensa ya dora a jikin ta kuma ya fara wasa da jikin nata a hankali, yana wansan yana cire mata kaya a hankali, yana wasa da cibiyarta kuma yana yin sama da hannun sa zuwa kirjinta a hankali, da zaran yakai hannusa a kan nononta, sai yaci gaba da wasa da nonowan n...

Gammamen Bayani AKan Layyah

◉ LAYYA [YANKA] ◉ Bismillahir Rahmanir Rahim: . Lallai bayani dangane da Layya tana da fad'i sosai amma zamu taqaita a taqaice. . ◉ LAYYA: ita ce dabbar da ake yankewa domin neman yardar ALLAH daga cikin nau'o'in tumaki da Awaki da Shanu da Raquma wad'anda suka cika shekarun yin layya, kuma sun ku6uta daga kowane aibi. .  →An shard'anta yanke dabbar layya a ranar 10 ga watan Zu-lhijjah da yini biyu masu bi mashi, bayan dawowa daga sallar idi, bayan kuma Liman ya yanke. [Fawakihud-dawaniy 1/440] . → Sheikh Abubakar Jaza'iriy ya fad'a acikin littafinsa mai suna [Minhajul Muslim] Yace: LAYYA wata dabba ce wadda ake yankewa ranar idi domin neman yardar ALLAH, ana yin ta ne don raya sunnar Annabi Ibrahim (AS) domin ALLAH Yayi wahayi zuwa gare shi da ya yanke d'anshi Isma'eel (AS), sannan kuma ya fanshe shi da Rago, ya Yanke shi a madadinsa. Kamar Yadda yazo acikin Alqur'ani ALLAH (SWT) Yace: . ﻭَﻓَﺪَﻳْﻨَﺎﻩُ ﺑِﺬِﺑْﺢٍ ﻋَﻈِﻴﻢٍ .  Ma'ana: "Kuma m...