Skip to main content

Wai Me Ke Kawo Saurin Mutuwar Aure


Allah abin godiya! Yau ga shi mun shigo wani zamani – musamman a kasar Hausa da mutuwar aure ba ta zamo wani babban al’amari da za a damu da shi ba. Al’amura sun sauya ba kamar zamanin baya ba, wato zamanin da kafin ka ji aure ya mutu, sai da wani kwakkwaran dalili; wanda idan kowa ya ji, ba zai ji a ransa cewa aure ya mutu cikin ganganci ba.

Kwanci-tashi al’amura suna sauyawa ta yadda a kullum matsalolin kara ta’azzara suke yi, maimakon raguwa. Daga cikin matsalolin da suke kara ta’azzara, akwai wanda na ambata a sama: saki.

A dabi’ance, kamata ya yi a ce da zarar mutum ya yi aure sai ya samu wani irin sauyi cikin rayuwarsa ta yadda zai sauya daga rashin samun natsuwa zuwa ga samun natsuwa, daga rashin kwanciyar hankali zuwa ga kwanciyar hankali, daga kunci zuwa farin ciki. Amma kash! Abin yanzu kwata-kwata ba haka ba ne – ya jirkice.

Wani ma yakan ji da bai yi auren ba saboda tsabar bala’in da ya tarar a ciki. Za mu iya cewa daga mata da miji zuwa iyayensu (watakila da ’yan uwansu), kowa yana da nasa laifin wajen mutuwar aure. Wasu lokutan, iyaye kan zama silar mutuwar aure tun kafin auren ta hanyar tsauwala wa mijin da ’yarsu za ta aura wajen sayen kayan lefe da biyan kudin sadaki.

A daidai wannan gaba, Malam Muhsin Ibrahim, mai sharhi kan al’amuran yau da kullum kuma malami a Jami’ar Cologne, ya dan tabo mana yadda lamarin yake a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook. Ya ce: “Wata ’yar uwata ta ban labarin wani aure da ta halatta. Angon sai da ya sayo akwatin lefe saiti 12.

A da, saiti 3 ake yi, sannan ya zamo 4, sannan 6, yanzu kuma 12! In da angon zai kawo kasa da haka, sai ’yan uwa da kawayen amaryar su koka, ba tare da la’akari da nauyin aljihunsa ba.” Malam Muhsin ya kara da jefo wasu ’yan tambayoyi:

Don Allah wace irin rayuwa muke son zaba wa kanmu ne? Me ya sa muke son tsauwala al’amura ga kawunanmu da gangan?” Ita wannan tsauwalar za ta kashe aure ne ta hanyar sanya miji ya rika ji a ransa kamar kudi ya zuba ya sayi matar.

Saboda haka, zai ji cewa duk abin da ya yi mata wanda ba daidai ba, babu bukatar ya ji ya yi mata kuskure. A haka sai zamantekawa ta rincabe. Sai kowa ya fara tauye wa kowa hakkinsa. Kafin ka ankara, aure ya mutu.

Kuma tsauwalar tana iya kawo rashin jituwa a tsakanin bangarorin biyu (wato bangaren amarya da na ango) bayan an yi aure. Hakan na saurin kashe aure ne domin shi mijin kullum zai rika kwana da tunanin cewa ba a tausaya masa ba lokacin da ya zo auren wannan yarinya.

Don haka, watakila, sai ya daina ganin kimar surukansa saboda ba su rangwanta masa ba. To ka ga ke nan tun daga nan an samu cikas. Wallahi tsauwalar ba ta da amfani. Saboda haka, don Allah, kowa – mace ko namiji, matashi da dattijo, mahaifi ko mahaifiya – ya yi kokari domin ganin ya bayar da gudunmawarsa wajen shawo kan wannan matsala domin ta shafi kowa.

Comments

Popular posts from this blog

YADDA AKE SADUWA DA AMARYA A RANAR FARKO!

Babban abinda yake sa Mata jin tsoron jama’i shine ta yadda ake fara saduwa dasu a lokacin da suka yi auren farko wato lokacin da aka aurar da yarinya tana budurwa. Abinda ya kamata mu sani anan shine lokacin da ango zai kawar da budurcin amaryar sa yakamata ya bita a hankali domin kada ya manta ita amaryar​ batasan yadda akeyin Jima’i ba. ,             YANDDA ANGO YAKAMATA YAYI YAYIN SADUWAR FARKO , An fi son miji yaje ma matarsa da hira kuma kada yayi gaggawar nuna mata cewar yin jimai ya kawo shi kusa da ita, ldan yana cikin hira da ita sai ya kwantar da kansa akan kafafuwanta kuma yaci gaba da hirar sa. , In an dan dauki lokaci ana hira sai ya dauki daya daga cikin hannayensa ya dora a jikin ta kuma ya fara wasa da jikin nata a hankali, yana wansan yana cire mata kaya a hankali, yana wasa da cibiyarta kuma yana yin sama da hannun sa zuwa kirjinta a hankali, da zaran yakai hannusa a kan nononta, sai yaci gaba da wasa da nonowan n...

Amfanin Ganyen Magarya A Jikin Dan’adam

Itaciyar ganyen magarya ana kiranta da Assidir a Larabce. Itaciya ce mai albarka da kuma dimbin tarihi.  Ya kasance ana amfani da ita tun kamin zuwan addinin Musulunci a duniya, bayan zuwan musulunci a duniya sai malamai da wasu magabata masana ilmin tsirran itatuwa suka bada fatawar amfaninta da irin cututtukan da take magani. Daga bisani suma masana kimiya ba a bar su a bayaba dan sun kaddamar da irin nasu bincike a kan alfanon ganye da kuma diyan magarya. Binciken ya baiwa masana ilimin harhada magani na yankunan turai da wasu yankunan kasahen duniya na Larabawa da India dama nan Afrika wata muhimmiyar damar saka bishiyar magarya a jerin bishiyoyin da ke da karfi da saurin warkar da wasu cututtukka. Ga kadan daga cikinsu:========= -Ciwon daji: A dafa garin magarya a misalin kofi daya karami sai a tarfa zuma mai kyau cokali biyu sai a sha da safe bayan an ci abinci. Amma a sanda ake shan magani irin wannan akwai bukatar a kauce wa shan wasu rukunnan magunnan bature. -Miki ko kura...

Yadda Zaka Gamsar Da Matan Ka

Dukkanmu mun taso mun samu ana cewa mata sun kasu gida uku game da lamarin kwanciya: akwai harija, mutawassida da dakhila. Ta tsakiyar ce ta fi yawa a rahotannin baka. Marubucin nan bai da tabbas game da wannan bayani a ilmance. Amma dai maganar ba ta yi nesa da abin da gogayyar yau da kullum take tabbatarwa ba. Gazawa ce a bangaren namiji, ko ma a wane rukuni matarsa ta fada a cikin biyun qarshen nan, a ce ba ya iya gamsar da ita a wurin kwanciya. Kazalika qalubale ne a gare shi, idan matar ta kasance cikin rukunin farko, dolensa ya zaqulo yadda zai gamsar da ita. To me da me ke sa mutum ya iya gamsarwar? Farko, akwai buqatar bahaushe ya gane cewa ba fa zallan dukhuli ne ke gamsar da mace ba, sai ya riqa hadawa da nau’in “romance” din da matar ke buqata. Mata da yawa na qorafin wannan jahilci nasa. Binciken masana harkar ya bayyana cewa, ko minti biyar kawai miji zai yi a duhuli, amma ya yi “romance” da matarsa na kimanin awa guda, za ta gamsu. Wane irin “romance” ne mata ke buqata? K...