Skip to main content

Yadda Buhari Yayi Murdiya Gurin Lashe Zaben 2019 Inji Ahmad Gumi


Babban Malamin addinin Islama, Sheikh Ahmad Gumi ya soki Shugaba Muhamadu Buhari bisa nasarar da ya samu na lashe zaben shugabancin kasa na 2019 da aka gudanar a ranar 23 ga watan Satumba kuma aka sanar da sakamakon zaben a ranar 27 ga watan Fabrairu.
Sheikh Gumi ya koka kan yadda Buhari ya yi gadarar cewa shine zai lashe zaben tun kafin a fara kirga kuri'u da al'umma suka kada.

Kamar yadda muka samu rahoto daga Daily Nigerian, Sheikh Gumi ya ce, "Tun kafin a kirga kuri'u, Shugaba Muhammadu Buhari ya yi imani 100% cewa shine zai lashe zabe. Ta yaya ya san shine zai lashe zaben duba da cewa kan 'yan kasar a rabe ta ke kuma ana fama da talauci da fatara????
Yace "Ba dai zai ce ayyukansa da cancantarsa bane suka sanya shi ya lashe zabe. Tattalin arziki, tsaro da rashawa duk sunyi katutu a kasar. Kasar na fama da karancin ayyukan yi, ana samun karuwar kashe-kashe na kabilu, ana samun karuwar sace mutane, talauci da rashawa a ko wane lungu da sako.
"Abinda kawai zai sanya shi ya bugi kirji ya ce shine zai lashe zabe itace karfin mulki da ya ke dashi a matsayinsa na shugaba wanda shi ake nufi da halastaciyar rashawa.

"Duba TraderMoni da aka kaddamar watanni kadan kafin zabe sannan ana amfani da EFCC wurin musguwanawa abokan hammaya, amfani da kudin gwamnati wurin shirya kamfe, mamaye gidajen talabijin da rediyo na gwamnati da kuma amfani da masallatai domin yin kamfen da amfani da sojoji domin razana masu zabe da sauransu, halastaciyar rashawar na da yawa." inji shi
Sheikh Gumi ya koka kan yadda jam'iyyar APC ta rika rabawa mata a kauyuka N500 domin su zabi APC tare da amfani yara wanda shekarunsu bai kai na zabe ba wurin kada kuri'a da kuma yim amfani da mimbarin malamai domin kamfe.
Babban malamin ya yabawa dan takarar shugabancin kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar saboda jajircewarsa. Ya kuma shawarce shi ya yi watsi da sakamakon zaben ya garzaya kotu domin a bi masa hakkinsa kamar yadda Shugaba Buhari ya yi a baya.
A karshe Ya kuma yi kira ga al'umma su cigaba da zama lafiya tare da biyayya ga doka da oda.

Comments

Popular posts from this blog

Amfanin Ganyen Magarya A Jikin Dan’adam

Itaciyar ganyen magarya ana kiranta da Assidir a Larabce. Itaciya ce mai albarka da kuma dimbin tarihi.  Ya kasance ana amfani da ita tun kamin zuwan addinin Musulunci a duniya, bayan zuwan musulunci a duniya sai malamai da wasu magabata masana ilmin tsirran itatuwa suka bada fatawar amfaninta da irin cututtukan da take magani. Daga bisani suma masana kimiya ba a bar su a bayaba dan sun kaddamar da irin nasu bincike a kan alfanon ganye da kuma diyan magarya. Binciken ya baiwa masana ilimin harhada magani na yankunan turai da wasu yankunan kasahen duniya na Larabawa da India dama nan Afrika wata muhimmiyar damar saka bishiyar magarya a jerin bishiyoyin da ke da karfi da saurin warkar da wasu cututtukka. Ga kadan daga cikinsu:========= -Ciwon daji: A dafa garin magarya a misalin kofi daya karami sai a tarfa zuma mai kyau cokali biyu sai a sha da safe bayan an ci abinci. Amma a sanda ake shan magani irin wannan akwai bukatar a kauce wa shan wasu rukunnan magunnan bature. -Miki ko kura...

YADDA AKE SADUWA DA AMARYA A RANAR FARKO!

Babban abinda yake sa Mata jin tsoron jama’i shine ta yadda ake fara saduwa dasu a lokacin da suka yi auren farko wato lokacin da aka aurar da yarinya tana budurwa. Abinda ya kamata mu sani anan shine lokacin da ango zai kawar da budurcin amaryar sa yakamata ya bita a hankali domin kada ya manta ita amaryar​ batasan yadda akeyin Jima’i ba. ,             YANDDA ANGO YAKAMATA YAYI YAYIN SADUWAR FARKO , An fi son miji yaje ma matarsa da hira kuma kada yayi gaggawar nuna mata cewar yin jimai ya kawo shi kusa da ita, ldan yana cikin hira da ita sai ya kwantar da kansa akan kafafuwanta kuma yaci gaba da hirar sa. , In an dan dauki lokaci ana hira sai ya dauki daya daga cikin hannayensa ya dora a jikin ta kuma ya fara wasa da jikin nata a hankali, yana wansan yana cire mata kaya a hankali, yana wasa da cibiyarta kuma yana yin sama da hannun sa zuwa kirjinta a hankali, da zaran yakai hannusa a kan nononta, sai yaci gaba da wasa da nonowan n...

Sirrin Samun Saurayi Nagari

Duk wata mace da ta gagara samun miji, to lallai akwai abun dubawa a kanta. A matsayin ta na mace ta taba kokarin samun namijin kirki amma bata samu ba? Ga wasu shawar’wari daga bakin masana. Idan har duk yadda kikayi wajen neman miji wanda yake sonki kuma yadamu da ke amma hakar bata cimma ruwa ba, to gwada wadannan abubuwan ki sha mamaki. A watan azumi da ake ciki, ki kokarta wajen kyautata dangantakarki da Allah, ki bada kyauta ga mabukata. Haka ki yawaita fara'a da nafilfilin dare, da rokon Allah ya kawo miki miji nagari da kuma dacewa da sa'a a wannan rayuwar. Ki rage yawan fada, da yawan surutu tsakanin ki da sauran 'yan uwa mata ko maza. Kada kuma azumi ya hanaki kwalliya da gyaran jiki, yadda ya kamata ace ko wace mace na yi. Kokarta wajen kamun kai, magana da kowane irin mutun, shiga harkar da bata shafe kiba, gulmar kawa ko aboki, yawaita bakinciki don kawarki nada saurayi, ke baki da shi. To fara duba kanki, ki gani wai me kikeyi wanda ya sabama yadd...